1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An bude taron kasa da kasa kan yaki da kyamar Yahudanci

Mohammad Nasiru AwalMarch 14, 2016

Taron da majalisar dokokin Jamus ta Bundestag ke karbar bakoncinsa yana samun halarcin wakilai fiye da 100 daga kasashe 40.

https://p.dw.com/p/1ID5P
Symbolbild Männer mit Kippa
Hoto: picture-alliance/dpa/B. Pedersen

Shugabar gwamnatin Jamus Angela Merkel ta ce kyamar Yahudanci da wariya ba su da wurin zama a kasar ta Jamus. Merkel ta yi wannan furuci ne a wani jawabin da ta gabatar lokacin bude taron majalisun kasa da kasa kan yaki da kyamar Yahudanci wanda majalisar dokokin Jamus ta Bundestag ke karbar bakoncinsa.

Ta ce: "A bayyana yake ga duk mazaunin Jamus da wanda ya jima a nan da ma bakin da ke shigo mana, cewa kyamar Yahudawa da nuna wa wani rukuni na al'umma wariya ba abu ne da za a aminta da shi a Jamus ba. Muna ganin kyamar Yahudanci a bangarori daban-daban na al'umma. Kai hari kan wuraren ibada daidai yake da keta hakkin dan Adam na yin addinin da ya ga dama."

Wakilan majalisun dokoki fiye da 100 daga kasashe kusan 40 ke halartar taron na yini biyu da za a kamma a ranar Talata.