1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An bude taron neman tsagaita wutar rikicin Ukraine

September 5, 2014

A birnin Minsk na kasar Belarussia wakilan tuntubar juna kan rikicin Ukraine sun fara taro yayin da ake gwabza fada a gabashin kasar.

https://p.dw.com/p/1D7hm
Ukraine Gespräche in Minsk 05.09.2014 Leonid Kutschma
Hoto: picture alliance/AP Photo

Wakilan tuntubar juna a kan Ukraine sun fara tattauna batun kawo karshe rikicin yankin. Wakilan kasar Rasha da na gwamnatin Ukraine da kuma na kungiyar tsaro da hadin kai a Turai tare da na 'yan aware suna gudanar da shawarwari a Minsk babban birnin kasar Belarussia a kokarin cimma shirin tsagaita wuta a rikicin gabashin Ukraine. Sai dai rahotanni na cewa duk da fara wannan taro, har yanzu ba a kai ga tsagaita wuta ba, inda a can gabashin Ukraine din ake ci gaba da gumurzu tsakanin dakarun gwamnati da na 'yan aware magoya bayan Rasha. Har yanzu kuma ana cikin halin rashin tabbas a Mariupol. Bayan da 'yan tawaye suka sanar da kame birnin, an jiyo kakakin rundunar sojin Ukraine na musanta wannan ikirari, yana cewa har yanzu birnin na hannun dakarun gwamnati.

Mawallafi: Mohammad Nasiru Awal
Edita: Suleiman Babayo