1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An hallaka ministan Falesdinu

December 10, 2014

Shugaban Falesdinawa Mahmud Abbas ya yi tir da kisan wani minista a gwamnatinsa da Isra'ila ta yi

https://p.dw.com/p/1E1zg
Ziad Abu Ain bei den Protesten bei Ramallah 10.12.2014
Hoto: AFP/Getty Images/A. Moman

Shugaban Falesdinawa Mahmud Abbas ya yi tir da kisan jami'in gwamnatinsa Ziad Abu Ain, da dakarun Isra'ila suka yi lokacin wata fafatawa a wannan Laraba.

Abbas ya ce za su dauki matakin gudanar da bincike sanain abin da ya faru. Shaidun gani da ido sun ce minista a gwamnatin Falesninawa Ziad Abu Ain dan shekaru 55 da haihuwa, ya rasa ransa lokacin da dakarun Isra'ila suka harba hayaki mai saka hawaye kan masu zanga-zanga a yankin Gaban Yamma da Kogin Jordan.

Mawallafi: Suleiman Babayo
Edita: Umaru Aliyu