1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Jamus: Masu kyamar baki sun farma 'yan kasar Guinea

August 2, 2020

A Jamus wasu mutane 'yan kasar Guinea su uku sun gamu da harin kyamar baki.

https://p.dw.com/p/3gHNz
Deutschland | Berlin | Black Lives Matter Protest
Hoto: picture-alliance/AA/A. Hosbas

'Yan sanda sun ce sun samu bayanan da suka tabbatar musu cewa an kai wa wadannan mutane hari ne a saboda launin fatarsu, kuma daya daga cikin mutanen da abin ya shafa ya ji rauni sosai.

A halin da ake ciki mutane ukun suna asibiti inda suke jinya. Tuni dai 'yan sanda suka sanar da kamen mutane 12 bayan harin na ranar Asabar da ya gudana a wani fitaccen dandalin taruwar masu ra'ayin kyamar baki a birnin  Erfurt. Masu shigar da kara su ma sun ce sun fara bincike a kan lamarin domin kwato wa mutanen hakkinsu.