An kama masu yunkurin juyin mulki a Burundi
May 15, 2015Talla
Yayin da yake magana ta wayar tarho da kanfanin dillancin labaran kasar Faransa na AFP Janar Niyombare ya ce sun amince su mika kansu inda ya ce sun kira ministan cikin gidan kasar da ma na tsaro inda suka sanar da su cewa basa dauke da makamai.
Tun dai a jiya ne janar Cyrille Ndayirukiye da ke a matsayin na hannun damar janar Niyombare, ya sanar cewa yunkurin nasu ya ci tura ganin yadda suka fuskanci jajircewa daga sojoji masu kare wannan gwamnati. Sakatare janar na Majalisar Dinkin Duniya Bam Ki Moon ya yi Allah wadai da yunkurin juyin mulkin inda ya yi kira da a dawo da kwanciyar hankali a wannan kasa.