1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An kama sojojin da suka kashe mata a Kamaru

July 19, 2018

Hukumonin Kamaru sun kama sojojin da suka kashe wasu mata da 'ya'yansu a yankin arewa mai nisa.

https://p.dw.com/p/31moy
Kamerun Amchide Polizei Spezial Soldaten Anti Boko Haram 07/2014
Hoto: Reinnier Kaze/AFP/Getty Images

Rahotannin da ke fitowa daga kasar Kamaru na cewa an cafke wasu sojoji hudu da aka yi zarginsu da kashe wasu mata biyu goye da 'ya'yansu biyu a yankin arewa mai nisa.

Wata majiyar tsaro ce ta tabbatar da wannan labarin, kamar yadda kamfanin dillancin labaran Reuters ya labarta.

Wani faifan bidiyo da ya fito a makon jiya, da kuma daruruwan dubban mutane suka yi ta gani, ya matukar tayar da hankalin al'umar duniya, inda aka yi ta kiraye-kirayen a dauki mataki.

Tunda fari dai kakakin gwamnatin kasar ta Kamaru Issa Tchiroma Bakary, ya musanta sahihancin labarin, koda ya ke ya amince cewar za a gudanar da bincike.

Wata majiyar ma ta tsaro, ta ce an ma aika uku daga cikin sojojin zuwa Yaounde babban birnin kasar, yayin da daya ke a garin Maroua.