An kama wani ƙusa na Boko Haram
July 15, 2014Talla
Mohammed Zakari mai kimanin shekaru 30 da haifuwa, an kama shi ne a wani farmaki da jami'an tsaro suka kai a kan hanyar garin Darazo da ke cikin jihar Bauchi da ke a yankin arewacin ƙasar.
Kakakin 'yan sandar na Najeriya Frank Mba,ya ce Zakari yana da hannu dumu-dumu a cikin kisa na yara ƙanana da mata a hare-haren da Ƙungiyar ta Boko Haram ta kai a yankuna da dama na arewacin ƙasar. Wannan kamu dai na zuwa ne a sa'ilin da ake ci gaba da samun ƙaruwar kai hare-haren na masu kishin addini a Najeriya.
Mawallafi: Abdourahamane Hassane
Edita : Suleiman Babayo