1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An kayyade yan takara takwas a Jamhuriyar Afirka ta tsakiya

January 19, 2014

Majalissar rikon kwaryar kasar Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya, ta kayyade yan takarar neman shugabancin rikon kwaryar kasar ga mutun takwas.

https://p.dw.com/p/1AtTv
Zentralafrikanische Republik Übergangsregierung
Hoto: Eric Feferberg/AFP/Getty Images

A wannan Litinin din dai majalissar za ta zabi shugaban da zai gaji Michel Djotodia, da yayi murabus bayan matsin kaimin da ya fuskanta a wani taron kasashen yankin, a kokarin da ake na magance rikicin kasar da yaki ci yaki cinye wa.

Daga cikin yan takarar dai akwai Magajiyar garin birnin Bangui Catherine Samba-Panza, da Désiré Kolingba dan tsofon shugaban kasar André Kolingba, da wani hamshakin dan kasuwa Sylvain Patassé, shima dan tsohon shugaban kasa Ange-Félix Patassé.

Shidai André Kolingba wanda janar ne na soja ya hau karagar mulkin kasar ne a 1981 bayan wani juyin mulki kuma ya jagoranci kasar har ya zuwa shekarar 1993 inda Ange-Félix Patassé ya kada shi a wani zabe da akayi na demokradiya kuma ya rasu ne birnin Faransa a shekara ta 2010, yayin da shi kuma Ange-Félix Patassé ya jagoranci kasar ta Jamhuriyar Afirka ta tsakiya a karo biyu kafin daga bisani François Bozizé ya tumbuke shi a wani juyin mulki a shekarar 2003 wanda shi ma ya rasu a kasar Kamaru a 2011.

Ana so dai du dan takara ya kasance bashi da wata alaka da yan kungiyar Seleka ta Musulmin kasar, da ma ta anti-Balaka mayakan sa kai mabiya adinin Kirista a wannan kasa.

Mawallafi: Salissou Boukari
Edita: Mohammad Nasiru Awal