1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An sako dan takarar shugabancin kasa a Tunisiya

Binta Aliyu Zurmi
October 9, 2019

Kotu a Tunusiya ta amince a saki dan takarar shugabancin kasar da aka yi a watan jiya, Nabil Karoui da ake tsare da shi. Nabil Karoui ne ya zo na biyu a zagayen farko na zaben. 

https://p.dw.com/p/3Qzxt
Tunesien Tunis | Medienmogul Nabil Karoui
Hoto: Getty Images/AFP/Hasna

Umurnin kotun na zuwa ne gabanin zaben shugaban kasar zagaye na biyu da za a gudanar a ranar Lahadi mai zuwa 13 ga wannan wata na Oktoba. 

Mahukuntan kasar ta Tunusiya sun kame Karoui a watan Agustan wannan shekara da muke ciki, bayan tuhumarsa da rashin biyan kudin haraji da kuma musayar kudi ba bisa ka'aida ba. 

Nabil Karoui mai shekaru 56 a duniya ya yi fice wajen sukar lamirin gwamnatin kasar ta wani gidan talabijin mai zaman kansa da ke zama mallakinsa.