1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An sako fursunonin siyasa 80 a Sudan

Abdul-raheem Hassan MNA
February 19, 2018

Gwamnatin shugaba Omar Hassan al-Bashir ya ba da umarnin sako fursunonin da aka kama lokacin zanga-zangar adawa da gwamnati a watan Janairu, inda aka tsare su a gidan yarin babban birnin kasar Khartoum.

https://p.dw.com/p/2suIy
Sudan Wiederwahl Präsident Omar al-Baschir
Hoto: Reuters/Str

A farkon shekarar 2018 jami'an tsaro suka kame mutane da dama ciki har da jagororin jam'iyyun adawa, yayin wata arangama da ta barke tsakanin 'yan sanda da fararen hula a lokacin gudanar da zanga-zangar nuna adawa da matsin tattalin arziki da hauhawar farashin kayan abinci.

Amma har yanzu ana ci gaba da tsare wasu jiga-jigan 'yan adawa, abin da ya sa jama'a suka yi ta rera wakokin 'yanci da taken kasar a gaban gidan yarin da nufin nuna matsin lamba ga gwamnati domin sako sauran mutanen da ake tsare da su.

A bara kasar Amirka ta janye wa Sudan takunkumin sama da shekaru 20, inda ta bukaci hukumar ba da lamuni ta duniya da ta yi wa Sudan sassauci a wani mataki na farfado da tattalin arzikinta.