1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Steinmeier ya yaba da matakin da Rasha ta dauka

Mohammad Nasiru AwalApril 15, 2015

Halin ya kamata da Rasha ta nuna ya kai ga zartas da kudurin sanya wa 'yan tawayen Yemen takunkumin sayar musu da makamai.

https://p.dw.com/p/1F8u2
Deutschland Treffen der G7 Außenminister in Lübeck PK Steinmeier
Hoto: Reuters/F. Bensch

Ministan harkokin wajen Jamus Frank-Walter Steinemier ya yi maraba da kudurin da Kwamitin Sulhun Majalisar Dinkin Duniya ya zartas,, inda ya sanya takunkumin sayar wa 'yan tawayen Houthi a kasar Yemen makamai. Steinmeier ya fada wa wani taron ministocin harkokin wajen kasashen kungiyar G7 da ke wakana a garin Lübeck na nan Jamus cewa wannan matakin ya samu ne saboda halin ya kamata da kasar Rasha ta nuna. Rasha dai ta yi rowar kuri'arta amma ba ta hau kujerar naki ba a lokacin kada kuri'ar amincewa da kudurin sanya wa 'yan Houthi takunkumi. A kan rikicin na Yemen Steinemier cewa ya yi.

"Bisa la'akari da halin da ake ciki a Yemen, za mu tattauna kan damarmakin da muke da su na kawo karshen wannan rikici, wanda ke kara yin muni yake kuma janyo asarar rayuka a kullum."

Taron zai kuma tattauna kan rikice-rikicen da ake fama da su a duniya baki daya da kuma batun kare muhalli da na sufurin jiragen ruwa.