1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An yi garkuwa da turawa a Najeriya

Ramatu Garba Baba
October 18, 2017

Rahotani da ke fitowa daga Najeriya na cewa wasu 'yan bindiga sun yi garkuwa da wasu turawan Britaniya hudu a jahar Delta dake a yankin Naija Delta na Kudancin kasar.

https://p.dw.com/p/2m7Tj
Nigeria Rebellengruppen im Nigerdelta
Hoto: picture-alliance/dpa

Kakakin 'yan sanda na jahar Delta Andrew Aniamaka ya tabbatar da labarin sace turawan inda ya ce wasu 'yan bindiga biyar ne suka yi awon gaba da su daga wani kauye a yayin da suke aikin kulawa da mutane  a yankin, ya kuma kara da cewa ba a ji duriyar 'yan bindigan ba kan neman kundin fansa ya zuwa lokacin da yake yi wa manema labarai jawabi.