1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An yi kira da a kara kai dauki ga yankunan girgizar kasa na Pakistan da Indiya

October 22, 2005
https://p.dw.com/p/BvON

Sakatare janar na MDD Kofi Annan ya sake yin kira ga kasashen duniya da su kara yawan taimako ga yankunan da ke fama da bala´in girgizar kasa a Pakisan da Indiya. A cikin wata wasika da ya aikewa gwamnatocin kasashe membobin MDD Kofi Annan ya ce dole a nunawa wadannan yankuna zumunci daidai da wanda aka nuna bayan igiyar ambaliyar ruwa ta Tsunami da ta auku a tekun Indiya. Annan ya ce yawan mutane da zasu mutu ka iya karuwa fiye da yadda ake zato idan ba´a kai taimakon gaggawa ba musamman yanzu da sanyin hunturun ke karatowa. Hukumomi a dukkan yankunan Kashmir da abin ya shafa sun ce mutane kimanin dubu 79 suka mutu. A kuma halin da ake ciki kungiyar tsaro ta NATO zata aike da sojoji kimanin dubu daya ciki har da likitoci da makanikai zuwa Pakistan. Yanzu haka dai ma´aikatan ceto na kokarin kaiwa ga wasu kauyuka dake kan tsaunuka inda har yanzu ba wani taimako da ya isa can.