1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Angela Merkel ta kare matsayinta kan 'yan gudun hijira

Kamaluddeen SaniMarch 12, 2016

A wani yunkuri a yayin gudanar yakin neman kamfen na karshe na zabubbukan 'yan majalisun dokokin jihohi uku da ke a Gabashin Jamus.

https://p.dw.com/p/1ICFE
Deutschland Angela Merkel Wahlkampfabschluss der CDU Baden-Württemberg
Hoto: Reuters/K. Pfaffenbach

Angela Merkel da ke zama shugabar gwamnatin kasar ta yi kokarin kare matsayinta t kan 'yan gudun hijira da ke ci gaba da shigowa kasar a inda ta ce:

''A wasu lokuta ya zama wajibi a dauki tsauraran hukunce-hukunce,a wani kaulin kusan dukkanin kasashen da ke a yankin Balkans sun taka rawa akan batun, kuma abubuwa masu tari yawa sun faru,yana da kyau mu koyi darasi daga kura-kuran da muka tafka a baya ta yadda abubuwa za su kai ga ingantuwa a gaba.''

Kazalika Shugabar ta kara da cewar mutane sun shigo mana kwatsam suna bukatar taimako idan muna da halin yin sai mutaima kesu:Angela Merkel dai na wadan nan kalaman ne a yayin ganagamin yakin neman zabe a Baden-Württemberg