1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Asarar rayuka a yake-yaken kasar Libiya

Salissou BoukariMay 21, 2015

An kashe sojoji da dama a wani sabon fada a kasar Libiya yayin da wasu kuma da dama suka samu raunuka a wannan kasa da ke fama da yakin basasa.

https://p.dw.com/p/1FTr5
Libyen Leben in Bengazi
Hoto: DW/M. Olivesi

Akalla sojoji goma sun rasu tun a ranar Laraba a wani dauki ba dadi da aka yi a birnin Bengazi, yayin da wasu 36 suka samu raunuka. Sannan kuma an kashe wani mayakin kungiyar Fajr Libiya a kusa da birnin Misrata a wani harin da kungiyar IS reshen kasar ta Libiya ta dauki alhakin kaishi.

Birnin na Bengazi da ke a matsayin cibiyar tada kayar baya a kasar ta Libiya, na fuskantar matsalar yake-yake tun bayan rushewar gwamnatin marigayi Moammar Kadhafi a shekarar 2011. A tsawon shekara guda fadan na Bengazi ya haddasa rasuwar mutane fiye da 1700 tare da ficewar wasu miliyoyin mutanen don tsira da rayukansu.