1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Rashin ci gaba ga matsalar bashin kasar Girka

Mohammad Nasiru AwalJune 22, 2015

Hukumomin lamuni na duniya da gwamnatin birnin Athens na kokarin cimma matsaya game da matalsar bashin kasar Girka.

https://p.dw.com/p/1FlpN
Deutschland EU Finanzministerrat in Brüssel
Hoto: Reuters/Y. Herman

Sai dai fatan samun wata maslaha na kara gushewa, gabanin wani taron koli na musamman da shugabannin kasashen Turai masu amfani da kudin bai-daya Euro za su yi da yammacin wannan Litinin a Brussles. Da rana an kammala wani taron ministocin ministocin kudi na kasashen kudin bai-daya na Euro ba tare da cimma wani sakamako ba. Taron dai ya kamata ya shirya taron kolin shugabannin. Wolfgang Schäuble shi ne ministan kudin Jamus ya yi karin haske.

Ya ce: "Kawo yanzu ba mu samu wasu shawarwari masu gamsarwa ba da za su zama madogara ga abin da ya kamata kungiyar kasashe masu amfani da kudin Euro su yi wato shirya wa taron kolin shugabannin Euro. Ba a samu wani canji ba tun ranar Alhamis da ta gabata."