1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Ban Ki-Moon ya kai ziyara a kasar Libiya

October 11, 2014

Sakatare Janar na Majalisar Dinkin Duniya ya isa a birnin Tripoli na kasar Libiya a wannan Asabar din, a wani mataki na karfafa tattaunawa tsakanin bengarorin kasar.

https://p.dw.com/p/1DTfJ
Hoto: Andrew Burton/Getty Images

Cikin wannan ziyara da ta kasance tamkar ta bazata, Ban Ki-Moon ya isa kai tsaye ne ga wani babban Otel da ke birnin na Tripoli domin tattaunawa da hukumomin wannan kasa a cewar wata majiya ta Majalisar Dinkin Duniya ta UNSMIL dake kasar ta Libiya.

A karshen watan Satumba ne dai da ya gabata, wakilin Majalisar Dinkin Duniya na musamman a wannan kasa Bernardino Leon, ya samu nassarar hada 'yan majalisu na bangarori daban-daban na wannan kasa a karo na farko, wanda ake ganin wani babbar ci gaba ne. A wannan ziyarar, Ban Ki-Moon yayi kira ga bengarorin kasar da su koma ga tattaunawa.

Mawallafi: Salissou Boukari
Edita : Pinado Abdu Waba