1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Birtaniya za ta kara tallafar NATO

Yusuf BalaJune 21, 2015

A cewar Ministan harkokin tsaron Birtaniya Fallon, ya zama wajibi a ci gaba da tura wa shugaban kasar ta Rasha Putin sakon cewa kasashen na NATO kansu a hade yake.

https://p.dw.com/p/1FkSU
Großbritannien Premierminister Cameron Immigration
Firaminista Cameron na BirtaniyaHoto: Reuters/M. Dunham

Birtaniya ta bayyana cewa a shirye take ta kara tallafin da ta ke bayarwa ga kungiyar tsaro ta NATO a kokarin samar da tsaro a yankin gabashin Turai ta hanyar kara wa'adin lokacin da dakarunta za su ci gaba da ayyukansu karkashin kungiyar.

Ministan harkokin tsaron Birtaniya Michael Fallon shi ya bayyana haka a ranar Lahadin nan.

Ana dai kara karfin sojin na kawancen NATO a yankin gabashin na Turai tun bayan zargin kasar Rasha da kokarin yin kutse a Ukraine, zargin da mahukuntan na birnin Masko ke karyatawa.

A cewar Ministan harkokin tsaron Birtaniya Fallon, ya zama wajibi a ci gaba da tura wa shugaban kasar ta Rasha Putin sakon cewa kasashen na NATO kansu a hade yake.