1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Boko Haram na ci gaba da kai farmaki

October 6, 2014

A Najeriya kungiyar Boko Haram da ke gwagwarmaya da makamai ta yanka wasu mutane bakwai a garin Ngamdu da ke jihar Borno a yankin arewa maso gabashin kasar.

https://p.dw.com/p/1DRFa
Hoto: picture-alliance/AP Photo

Shaidun gani da ido Musa Abor da kuma wani jami'in gwamnatin jihar ta Borno da ya nemi a sakaye sunansa sun shaidawa manema labarai cewa sun fito da safe sunga gawarwakin mutanen bakwai an yi musu yankan rago. Shima wani jami'in tsaro a yankin da ya nemi a boye sunansa ya ce makwanni biyun da suka gabata sunyi arangama da 'yan Boko Haram din a garin Ngamdu inda suka hallaka kimanin 15 daga cikinsu wanda ya ce hakan ya sanya sun sha alwashin daukar fansa a kan al'ummar garin.

Ana dai kallon kisan wadannan mutane bakwai da kungiyar ta Boko Haram ta yi a matsayin ramuwar gayya ga kashesu da jami'an tsaron Najeriyar suke yi a 'yan kwanakin nan. Hare-haren kungiyar ta Boko Haram dai ya hallaka sama da mutane 10,000 tun bayan da aka fara shi a shekara ta 2009 kawo yanzu.

Mawallafiya: Lateefa Mustapha Ja'afar
Edita: Suleiman Babayo