1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Najeriya: Boko Haram ta kai hari a Kondiga

Abdoulaye Mamane Amadou
July 31, 2019

A Najeriya wasu yan bindiga da ake kyautata zaton mayakan kungiyar Boko Haram ne sun kai hari a wani kauye da ke jihar Borno a Arewa maso Gabashin Najeriya tare da hallaka mutane da kona gidajen jama'a.

https://p.dw.com/p/3N5SV
DW Still Boko Haram kill 65 people at funeral in Nigeria

Mayakan Kungiyar Boko Haram sun hallaka wasu mutane biyu tare jikkata wasu jama’a  da dama a wani harin da su kai a kauye Jakana da ke karamar hukumar Konduga mai tazarar kilomita 40 daga Maiduguri a Arewa maso Gabashin Najeriya. Rahotanni daga yankin sun ce mayakan sun kuma sace mutane ciki har da mata da matasa tare da kwasar kayan abinci da kona gidaje da shagunan jama’a da wasu kaddarorin gwamnati. Wani daga cikin masu aiyukan jinkai a yakin Malam Abdul’aziz Mala ya bayyana wa wakilinmu na yankin cewa jama’a na cikin fargaba. Kungiyar Boko Haram dai ta kara zafafa hare-harenta a ‘yan kwanakin nan inda ko a karshen makon da ya gabata mayakan suka hallaka mutane sama da 60 a Jihar ta Borno da ke Arewa maso Gabashin Kasar.