1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Boko Haram ta kai sabon hari a Najeriya

Binta Aliyu Zurmi
August 1, 2019

Rahotanni daga Najeriya sun tabbatar da wani hari da mayakan Boko Haram suka kai a yankin tafkin Chadi inda aka yi asarar rayuka. Lamarin dai ya shafi jami'an tsaro.

https://p.dw.com/p/3NBuh
Boko Haram
Hoto: Java

Wani fada da ya barke tsakanin sojoji da mayakan kungiyar Boko Haram da ke da alaka da IS a yankin arewa maso gabashin Najeriya ya yi sanadiyar mutuwar sojoji 25 da kuma a kalla mayakan na Boko haram 40. 


Kamfanin dillancin labarai na AFP ya ruwaito cewar wani kwamandan soji da ke a yankin ya ce mayakan na bangaren ISWAP sun kai harin ne a wani barikin soji da ke garin Baga a gabar tafkin Chadi inda gumurzu ya yi sanadin asarar rayuka daga bangarorin biyu.