1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Boko Haram ta kashe mutane 65 a Borno

Abdul-raheem Hassan
July 29, 2019

Maharan a kan babura da motoci sun bude wuta ne kan mutanen da ke dawowa daga jana'iza kuma harin ya jikkata wasu da dama. Wannan dai shi ne hari mafi muni kan fararen hula a baya-bayannan.

https://p.dw.com/p/3MsFZ
Nigeria 65 Menschen von Islamisten der Gruppe Boko Haram getötet
Hoto: AFP/A. Marte

Akalla mutane 65 ne aka tabbatar da mutuwarsu a sabon harin da ake zargin mayakan Boko Haram ne suka kaddamar a jihar Borno da ke Arewa maso gabashin Najeriya.

Babu kungiyar da ta dauki alhakin harin sai dai mayakan Boko Haram sun sha kai makamancin wannan mumunan hari kan fararen hula da jami'an tsaron Najeriya. Harin ya zo ne a lokacin da ake cika shekaru da fara rikicin Boko Haram a kasar. Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya yi Allah wadai da harin.