1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Buhari: Muna jinjina wa China kan tallafi

Kamaluddeen SaniApril 12, 2016

Shugaban kasar China Xi Jinping ya tabbatar wa tarayyar Najeriya hadin kan kasarsa a bangarorin masu tarin yawa, a yayin da ya gana da Shugaba Muhammadu Buhari.

https://p.dw.com/p/1IUBR
Muhammadu Buhari Präsident Nigeria Porträt G7 Gipfel 2015 Schloss Elmau
Hoto: picture-alliance/dpa/Minkoff

Xi Jinping ya ce shekara ta 2016 na kasancewa shekaru 45 cif da kulla dangantakar diplomasiya tsakanin China da Najeriya, kuma dukkanin kasashen sun ribaci dangantaka mai gwabi a tsakaninsu a bangarori da dama.

Kazalika Shugaban kasar China ya ce a shirye suke su kara kulla danganta da Najeriya a fannonin Ayyukan noma, kifi, matatun man fetur,da ma'adanan karkashin kasa gami da bunkasa harkokin masana'antu. 

Ana sa bangaren Shugaba Muhammadu Buhari ya jinjina wa China a bisa irin tallafin da kasar take baiwa Najeriya wajen habaka harkokin ci gaba.

Dukkanin shugabanin biyu sun rattaba hannu a kan wasu yarjeniyoyi masu dama ciki har da noma da sanya hannayen jari.