1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An kai hari a Coci a Burkina Faso

Ramatu Garba Baba
May 13, 2019

'Yan bindiga sun kai hari a wata Cocin Katolika inda suka kashe limamin cocin da mabiya biyar. Maharan sama da 20 sun yi dirar mikiya a ginin, inda suka yi mata kawanya kafin su bude wuta kan mutanen da ke ibada.

https://p.dw.com/p/3IOp3
Burkina Faso Tag nach dem Angriff in der Kwame Nkrumah Avenue in Ouagadougou
Hoto: picture-alliance/abaca/AA/O. De Maismont

Magajin garin mai suna Dablo ya ce 'yan bindigar ba su bar wurin ba, sai da suka cinnawa ginin da wasu shaguna da ke harabar cocin wuta, tare da kona motar wata jami'ar lafiya. Harin da aka kai a karshen mako ya haifar da rudani a tsakanin mazauna yankin. Makwanni biyu da suka gabata ma dai, 'yan bindiga a kan babura sun kai hari kan Cocin Pentecostal, inda suka hallaka limamin cocin da mabiyansa biyar. Burkina Faso na daga cikin kasashen yankin Sahel da ke fama da ayyukan mayakan jihadi.