1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Burkina Faso gwamnati ta yi gargadi

Abdourahamane Hassane
November 25, 2020

Hukumomi a Burkina Faso sun yi kashedi ga duk wanda zai iya kawo yamutsi a cikin kasar daidai lokacin da ake dakon hukumar zabe ta bayyana sakamakon zaben kasar.

https://p.dw.com/p/3lojO
Burkina Faso Wahlen 2020 | Zephirin Diabre
Zéphirin Diabré jagoran 'yan adawaHoto: Katrin Gänsler/DW

Hakan kuwa ya biyo bayan sanarwar da 'yan adawar kasar suka bayyana na cewar an tafka magudi a zaben shugaban kasa da na 'yan majalisun dokokin da aka gudanar ranar Lahadin da ta gabata wanda suka yi brazanar cewar ba za su amince ba da sakamakon zaben. A cikin wata sanarwa da minista yada labarai na Burkina Fason Remi Fulgance ya bayyana ya ce gwamnati ba za  taba amincewa ba da tada zauna tsaye.