Chadi ta ce ba ta da hannu a rikicin Afirka Ta Tsakiya
April 4, 2013Gwamnatin kasar Chadi ta yi watsi - da kakkausar lafazi dangane da zarge zargen da hambararren shugaban jamhuriyyar Afirka Ta Tsakiya Francoir Bozize yayi na cewar, ta taimakawa kungiyar 'yan tawayen Seleka, wadanda suka kifar da gwamnatinsa kimanin kwanaki 10 da suka gabata. A cikin wata sanarwar da gwamnatin kasar ta Chadi ta fitar a wannan Alhamis (04.04.2013), ta ambata cewar: Tsohon shugaba Bozize ya gabatar da muhimman zarge zargen da gwamnatin Chadi ke yin watsi da su domin kuwa babu wani kamshin gaskiya a cikinsu.
Idan za ku iya tunawa dai tsohon shugaban jamhuriyyar Afirka Ta Tsakiya Farancoir Bozize ya nemi mafaka a jamhuriyyar Kamaru da ke makwabtaka da kasarsa, bayan kifar da gwamnatinsa, inda a wani taron sHugabannin yankin daya gudana a kasar Chadi a wannan Larabar (03.04.2013), shugaba Idris Deby na kasar Chadi ya bukaci jamhuriyyar Bini ta baiwa tsohon shugaba Bozize mafakar siyasa.
Mawallafi : Saleh Umar Saleh
Edita : Usman Shehu Usman