1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Beijing ta yi martani ga NATO

Abdul-raheem Hassan
June 30, 2022

Kungiyar tsaro ta NATO ta bayyana kasar Sin a matsayin daya daga cikin manyan tsare-tsare a karon farko, tana mai cewa burin Beijing da manufofinta na kalubalantar tsaro da dabi'un kasashen yamma.

https://p.dw.com/p/4DTYR
China | Zhao Lijian
Zhao Lijian, kakakin ma'aikatar harkokin wajen ChinaHoto: Greg Baker/AFP/Getty Images

Gwamnatin China, ta yi kakkausar maratani ga kungiyar tsaro ta NATO, tare da cewa kungiyar ta tafka babban kuskure na yi mata mumunar fassara na ayyana Beijin a mastayin barazana.

Wannan dai shi ne karon farko cikin shekaru 10, da kungiyar NATO da ke taro a Spain ta ayyana Sin a matsayin karfen kafa.  Zhao Lijian kakakin ma'aikatar harkokin wajen China, ya ce NATO ta bata manufufiofin Beijing.

"Nato ta yi kalamai mara dadi kan ci gaban soja da manufofin tsaron kasa na Sin, wannan da dai-dai ba ne, zai kara haddasa tashin hankali ne, kuma yana cike da tunanin yakin cacar baka da kyamar akida."