1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Cika shekaru biyu da hawan mulkin shugaba Issoufou na Nijar

April 7, 2013

A yayin da shugaba Mahamadou Isoufou ya ce gwamnatinsa tana aiki tukuru don cika alkawuran da ta dauka, wasu 'yan kasar sun nuna rashin gamsuwarsu ga yadda yake tafiyar da mulki.

https://p.dw.com/p/18BEn
epa03142091 President of Niger, Mahamadou Issoufou delivers a speech during the opening ceremony of the 6th World water forum at Parc Chanot in Marseille, southern France, 12 March 2012. More than 1,000 high-level stakeholders are gathered in Marseille to share solutions to worldwide water problems and commit themselves to their implementation. EPA/GUILLAUME HORCAJUELO +++(c) dpa - Bildfunk+++
Hoto: picture-alliance/dpa

A jamhuriyar Nijar a ranar bakwai ga watan Afrilu aka yi shagulgulan bikin zagayowar shekaru biyu da hawan mulkin shugaban kasar Alhaji Mahamadou Isoufou. Albarkacin zagayowar wannan ranar, shugaban ya yi wa al'umma kasa jawabi, inda ya yi bitar aikin da ya yi na cika alkawuran da ya dauka.

Batun tsaro shi ne goshin jawabin da na sa, inda ya ce gwamnatinsa ta yi kokarin tabbatar da tsaro cikin gida, waje, bayan tashe-tashen hankulan da suka taso a cikin kasashen da makwabtan Nijar. Kasar da na cikin sahun kasashen da suka aika dakaru Mali, don fatattakar masu kishin addini da suka mamaye arewacin kasar. Bagu da kari gwamnatinsa ta dau matakin bai wa dakarun Nijar kayan aiki don kare iyakar kasar da kuma tabbatar da tsaro cikin gida. A tsari sa na dan kasa ya ci da dan kasa, shugaban ya ce gwamnatinsa na kokarin bunkasa noman fadama da kuma kiwon zamani ta yadda za a sami isasshen abinci. Kiwon lafiya da bunkasa ilimi da wadatar da ruwan sha gwamnatinsa na cikin cika alkawalin da ta dauka. A fannin hako ma'adani na karkashin kasa, tun lokacin da aka fara hako man fetur, an sami rarar kudi CFA miliyan dubu tasa'in da biyar. Wajen fara babban aikin hako karfen uranium a Umiraren wanda zai fara a 2015.

Rashin gamsuwa da wannan mulki

A nasu wajen 'yan adawa sun bayyana cewa tsawon shekaru biyu da shugaba Issoufu, ya yi a kan mulki bai yi wani aiki na a zo a gani ba. Mahaman Murtala, wani jigo a jam'iyar MNSD adawa, yace "batun tsaro dai babu wani ci gaba, inda ya musanta cewa ana ba duk soja tufafi kaya uku, ko kusa ba haka ba ne, daya ne ake ba ko wane soja. Sabanin mulkin tsohon shugaban kasa Tanja Mahamadou."

Titel: Seini Oumarou, Vorsitzender der Partei MNSD im Niger Schlagworte: Niger, Oumarou, Opposition, MNSD Wer hat das Bild gemacht?: offizielles Bild (MNSD) Wann wurde das Bild gemacht?: 2013 Wo wurde das Bild aufgenommen?: Niamey, Niger Bildbeschreibung: Bei welcher Gelegenheit / in welcher Situation wurde das Bild aufgenommen? Wer oder was ist auf dem Bild zu sehen? Seini Oumarou ist Vorsitzender der Partei MNSD-Nassara (Mouvement National de la Société de Développement ) und seit April 2011 Oppositionsführer im Niger. Zuvor hatte er in der Stichwahl um die Präsidentschaft gegen Mahamadou Issoufou verloren.
Seini Oumarou na jam'iyar MNSDHoto: MNSD

Murtalan ya ci da cewa gidajen asibitocin Nijar akwai matsaloli ga tsadar rayuwa, inda a yanzu ake sayar da buhun gero kudi CFA 30.000. Abinda ba a taba gani a Nijar ba.

A bangaren musu mulki a cewar Alhaji Adaye, mashawarci a fadar shugaban kasa, shi ganau ne ba jiyau ba alkawuran da shugaba ya dauka ya na cikasu.

"Can jihar Tahoua an sa mutanen kasar China, suna aikin saka fonfunan ruwa cikin karkara."

###ACHTUNG! NUR ZUR MIT DEM COPYRIGHTINHABER ABGESPROCHENEN BERICHTERSTATTUNG VERWENDEN### Resource ID 71175 Access Open Region West Africa Country Niger SCO 1.1 Food & Income Security Area of Work Disaster Risk Reduction Campaign Climate Change, GROW Humanitarian Crisis Drought, Food Crisis Classification Humanitarian Date 08 March 12 Credit Fatoumata DIABATE Copyright Fatoumata Diabate Caption Workers on the cash for work scheme. Programme Information Cash for work programme in the village of Gobro, Departement of Tibiri, region of Dosso, 1000 km east from Niamey The project is run in partnership with World Food Programme and Oxfam's partner NGO Mooriben. In exchange for cash (1000 XOF per day), beneficiaries are investing in the recuperation of land for agriculture. Schemes providing cash in exchange for work on community projects are one way Oxfam and partners keep food accessible for the most vulnerable while helping to protect markets. Oxfam invests in 'cash-for-work' projects and other cash initiatives, so that people have access to food on markets and markets are not distorted by food aid. In Niger, even in time of food shortage, the issue is more often related to access to food because of deep poverty and lack of financial resources or high prices, rather than to the unavailability of food on the market. In response to the current crisis, Oxfam and its partners are planning to help 450,000 people with vital aid such as food, cash, support to livestock, water, sanitation and hygiene promotion campaigns. In total, more than million people are facing a severe risk of food crisis in Niger. Specifically, in response to the influx of 30,000+ people from Mali, Oxfam and its partners are working to respond to the needs of refugees and host communities in the following sectors: food security, water, hygiene and sanitation, education and protection against gender-based violence. --------- Oxfam-Einverständniserklärung zugeliefert von Anne Le Touzé
Har yanzu ana fama da karancin abinci a wasu yankunan NijarHoto: Fatoumata Diabate/Oxfam

Har yanzu wasu ba su gani a kasa ba

To amma a bangaren ma'aikata sun bayyana rashin cika alkawarin wannan gwamnati tun hawan shugaba Mahamadou Issoufou. Kawancen mayan kungiyoyin kwadago wadanda suka yi gwagwarmayar kawo goyon bayan gwamnatin jamhoriya ta bakwai sun fiddo sanarwar sukan lamiri da kakkausar murya. Isoufu Sidiben shi ne babban sakataren babbar kungiyar dake jagoran kawancen kungiyoyin cewa yayi.

"A cikin shekaru biyu sun sa hannu an kulla yarjeniyoyi biyu amma ba su biya musu bukata ko daya ba. Kuma ba don sun yi zaman kawo ma wannan gwamnatin goyon baya ba, za su juya su yadda suka ga dama."

Mawallafi: Mahaman Kanta
Edita: Mohammad Nasiru Awal