1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Ebola ta sake ɓulla a Saliyio

Abdourahamane HassaneApril 7, 2015

Hukumomin kiwon lafiya sun ce wani jariri ya mutu da cutar Ebola a gabashin ƙasar a garin Kailahun.

https://p.dw.com/p/1F3P0
UNICEF Botschafter Orlando Bloom in Liberia
Hoto: picture-alliance/dpa/UNICEF

Tun can da farko gwamnatin ta ba da sanarwar cewar an kakape cutar daga yakin bayan da aka shafe watanni uku babu wani sabon kamuwa da cutar. Gwamnatin ta Saliyio ta ce ta killace iyaye da kuma na kusa da jaririn, sannan Ƙungiyar lafiya ta duniya WHO ta ce ta aike da wata tawaga domin tanttance dukkanin mutane da suka yi hulɗa da jaririn.

Hakan kuwa na zuwa ne a daidai da ake gudanar bukukuwan ranar kiwon lafiya ta duniya a yau bakwai ga watan Afrilu. Kawo yanzu, cutar ta Ebola wacce ta fara bazuwa a Gini a shekarun 2013 kafin ta isa a Laberiya da Saliyion,ta kashe sama da mutane dubu goma a cikin ƙasashen uku na yankin yammacin Afirka.