1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

ECOWAS za ta gudanar da taro kan Burkina

Abdourahamane HassaneNovember 5, 2014

Za a gudanar da zaɓen shugaban ƙasa a Burkina Faso a baɗi,a ƙarshen wa'adin mulkin shekara guda na gwamnatin riƙon ƙwarya.

https://p.dw.com/p/1Di2l
Westafrikanische Präsidenten fordern zivile Regierung in Burkina Faso 05.11.2014
Hoto: AFP/Getty Images/I. Sanogo

Shugaban ƙasar Ghana john Mahama Dramani kana shugaban Ƙungiyar gamayya tattalin arziki ta ƙasashen yankin yammacin Afirka wato ECOWAS.

Ya ce gwamnatin riƙon ƙwarya da za a girka a nan gaba a Burkina Faso za ta ɗauki tsawon wa'adin shekara guda,sannan ya ce za a gudanar da zaɓen shugaban ƙasa a cikin watan Nuwanba na shekarar baɗi kamar yadda aka tsara. A gobe Alhamis aka shirya Ƙungiyar ECOWAS za ta yi wani taro na musammun domin tattauna batun na Burkina Faso.