1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

EU ta bukaci a sake 'yan jaridu a Myanmar

Abdul-raheem Hassan
January 10, 2018

Kungiyar Tarayyar Turai ta yi Allah wadai da matakin hukumomin kasar Myanmar na ci gaba da tsare wakilan kanfanin dillacin labarun Reuters guda biyu, inda ta ce a gaggauta sakosu 'yan jaridun.

https://p.dw.com/p/2qcwc
Myanmar Reuters Journalisten vor Gericht Demonstranten
Hoto: Reuters

Matakin na kungiyar EU ya zo ne bayan da wata kotu a birnin Yangon ta zargi 'yan jaridun biyu da leken asiri. Hukuncin da kotun ta yanke ta yi amfani da kundin tsarin da ya ba da umarnin daurin shekaru 14 a kurkuku ga masu aikata laifukan leken asirin kasa.

An dai kama Wa Lone da kyaw Soe Oo a ranar 12 ga watan Disamba na shekarar 2017 bayan da wasu 'yan sanda biyu suka gayyacesu liyafar cin abinci, sannan suka kwace wasu kundin bayanai. 'Yan jaridun sun soki matakan gwamnatin Myanmar na neman boye gaskiyar al'amarin da ya faru a yakin jihar Rakhine.