1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

EU ta jinginar da batun sanya wa Rasha sabbin takunkumai

February 9, 2015

A taron da suka gudanar a birnin Brussels ministocin kudi na kungiyar EU sun ce za a jira sakamakon taron birnin Minsk kafin a san matakan da za a dauka gaba.

https://p.dw.com/p/1EYl4
EU Außenminister Treffen Brüssel Belgien
Hoto: picture-alliance/dpa/Olivier Hoslet

Ministocin harkokin wajen kasashen kungiyar tarayyar Turai sun ce ba za a kakaba wa Rasha sabbin takunkumai yanzu ba. A wani taron da suka yi a birnin Brussels ministocin sun ce ya kamata a jira sakamakon taron kolin da zai gudana wannan Larabar a birnin Minsk na kasar Belarus, inda shugabannin kasashen Rasha da Ukraine da Jamus da kuma Faransa za su duba batun tsagaita bude wuta a rikicin gabashin Ukraine. Frank-Walter Steinemeier shi ne ministan harkokin wajen Jamus cewa yayi.

"Ana ci gaba da shirye-shiryen gudanar da taron birnin Minsk. Muna fata taron zai gano bakin zaren warware batutuwan da ke hana ruwa gudu."

Sai dai da farko ministocin sun amince a kara sunayen wasu mutane 19 a jerin wadanda EU ta sanya wa takunkumi. Ana zarginsu da tallafa wa 'yan aware magoya bayan Rasha a gabashin Ukraine.

Mawallafi: Mohammad Nasiru Awal
Edita: Suleiman Babayo