1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

EU ta aminta da kara wa Rasha takunkumi

Yusuf BalaDecember 18, 2015

Za dai a cimma matsaya ta karshe kan wannan yarjejeniyar kara tsayin takunkumin kan Rashar nan ba da dadewa ba, wanda kuma za a wallafa a kan mujallar kungiyar ta EU.

https://p.dw.com/p/1HQGh
Belgien EU Gipfel Gruppenbild
Mahalarta taron EUHoto: Getty Images/D. Mouhtaropoulos

Jakadu daga kungiyar hadin kan Turai ta EU sun cimma matsaya wacce za ta bada dama a kara tsawon wa'adi na takunkumin tattalin arziki da aka kakabawa kasar Rasha da karin watanni shida anan gaba kamar yadda wani jami'in diplomasiya ya bayyana a ranar Juma'an nan bisa sharadin ba za a bayyana sunansa ba. Wannan dai na zuwa ne bayan tsaiko da aka samu a ci gaban yarjejeniyar tsagaita wuta a Gabashin Ukraine.

Daga nan zuwa ranar Talata ne dai za a cimma matsaya ta karshe kan wannan yarjejeniyar kara tsayin takunkumin kan Rashar, wanda kuma za a wallafa a kan mujallar kungiyar ta EU a cewar wannan jami'i. An dai kakaba wa kasar ta Rasha takunkumi na tattalin arziki tun a watan Yuli na shekarar 2014 saboda mamayarta a yankin Kiremiya da ma tsoma bakinta a rikicin Gabashin Ukraine.

Wannan takunkumi dai da kasashen na EU suka kakaba wa Rasha na sanyawa dukkanin bangarorin biyu na ji a jikinsu kan batun da ya shafi tattalin arziki.