1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

EU za ta sake tattaunawa kan Girka

Englisch-redFebruary 20, 2015

Ministocin kuɗi na Ƙungiyar Tarrayar Turai za su sake tattaunawa a karo na uku a Brussels a kan batun Girka.

https://p.dw.com/p/1Eetc
Tsipras Alexis Griechenland Parlament Athen Ministerpräsident Syriza
Tsipras Alexis firaministan GirkaHoto: picture alliance

Ana sa ran cimma daidaito a kan tsawaita shirin ba da tallafin kuɗaɗe ga ƙasar Girka wacce ke barazanar faɗawa cikin wani hali na rashin tabbas idan har ba cimma matsaya ba.

Firaministan na Girka Alexis Tsipras ya buƙaci a ƙara wa'adin tallafin da watannin shida. Sai dai Jamus ta yi karan tsaye kan cewar tilas ne Girkan ta ci gaba da aiwatar da shirin tsuke bakin aljihu kafin samun tallafin na biliyan 240.

Mawallafi : Abdourahamane Hassane
Edita : Usman Shehu Usman