1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Falasdinu ta kira wasu jakadunta su dawo

Zulaiha Abubakar
May 16, 2018

Umarnin ya biyo bayan rawar da wasu kasashe hudu wadanda suka hada da kasar Austiraliya da Chzech da Hungary da kuma Romaniya suka taka ne yayin mayar da Ofishin jakadancin kasar Amirka birnin Kudus

https://p.dw.com/p/2xpAK
USA UN Sicherheitsrat Mahmoud Abbas
Hoto: picture-alliance/dpa/AP ImagesM. Altaffer

Kasashen hudu dai sun ware daga cikin tawagar manyan kasashen Turai wadanda suka ki aikewa da wakilansu a ranar lahadin da ta gabata yayin bikin tarbar wakilan Amirka don bude Ofishin Jakadancinta da aka gudanar a ranar Litinin.

Kungiyar Tarayyar Turai ta soki ayyana birnin na Kudus da shugaba Donald Trump yayi a matsayin babban birnin kasar Isra'ila tare kuma da mayar da ofishin jakadancin Amirkar zuwa birnin na Kudus.