1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Sall ya bukaci kungiyar AU ta tsayar da yakin Libiya

Abdul-raheem Hassan MNA
January 29, 2020

Shugaba Macky Sall na kasar Senegal ya bayyana fargabar yaduwar makamai zuwa wasu kasashen yankin Sahel, muddin kungiyar tarayyar Afirka AU ta gaza daukar matakan gaggawa na kawo karshen yaki a Libiya.

https://p.dw.com/p/3Wx49
Libyen Tripoli 2019 | Kämpfer der GNA
Hoto: picture-alliance/Xinhua News Agency

Da yake jawabi yayin ganawarsa da Shugaban kasar Turkiyya Raccep Tayyip Erdogan a Dakar babban birnin kasar Senegal, Shugaba Macky Sall ya ce ilahirin nahiyar Afirka na cikin damuwa kan yadda ake gwabza fada a Libiya.

Shugaban na Senegal ya bukaci daukacin kasashen Afirka su samar da mafita kan halin da Libiya ke ciki, yayin ganawar da za su yi a Jamhuriyar Dimukuradiyyar Kwango.

Kasar Libiya na cikin rudani tun 2011 bayan kashe tsohon Shugaban kasar Kanar Moamar Gaddafi, inda ake yaki tsakanin gwamnatin hadin kan kasa da duniya ta amince da ita, wadda kuma Turkiyyar ke marawa baya da madugun adawa janar Khalifa Haftar kan iko da babban birnin kasar Tripoli.