1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Fatan warware rikicin nukiliyar Iran

November 20, 2013

Bayan tsawon shekaru na takaddama, a yanzu duniya na fatan ganin an warware rikicin nukiliyar Iran yayin sabuwar tattaunawa a birnin Geneva.

https://p.dw.com/p/1AL9X
U.S. Secretary of State John Kerry (2nd L), EU foreign policy chief Catherine Ashton (C), and Iranian Foreign Minister Mohammad Javad Zarif (2nd R) attend the third day of closed-door nuclear talks at the Intercontinental Hotel in Geneva November 9, 2013. France warned of serious stumbling blocks to a long-sought deal on Iran's nuclear programme as foreign ministers from Tehran and six world powers extended high-stakes negotiations into a third day on Saturday to end a decade-old standoff. REUTERS/Jean-Christophe Bott/Pool (SWITZERLAND - Tags: POLITICS ENERGY)
Hoto: Reuters/Jean-Christophe Bott

Iran da kasashen da ke da karfin fada a ji a duniya za su sake komawa ga tattauna batun nukiliyarta a birnin Geneva - a wannan Larabar, a kokarin da suke yi na cimma maslaha dangane da takaddama bisa shirin nukiliyar kasar ta Iran, da kuma shawo kan dari-darin da masu tsattsauran ra'ayi a Isra'ila da Amirka da kuma Iran ke da shi. Shugaban Amirka Barak Obama ya gana da jiga-jigai a majalisar dattijan kasar domin shawo kansu game da kaucewa sanyawa Iran karin takunkumi, wanda ka iya jefa tattaunawar diflomasiyyar cikin matsala, kana da sanya Iran cikin yanayin da za ta fadada shirin nukiiliyarta bayan dakatarwar da ta yi na wani dan lokaci. Ministan harkokin wajen Iran Mohammad Javad Zarif, ya aike da sako ta shafin yanar gizo na You Tube gabannin taron, inda ya fadi a birnin Roma na kasar Italiya cewar, akwai yiwuwar cimma nasara. Sai dai kuma shugaba Obama na Amirka ya shaidawa wata mujallar Amirka cewar, ba shi cikakkiyar masaniyar ko za a iya cimma yarjejeniya, ko dai a makonnan ko kuma a mako mai zuwa ne.

Mawallafi : Saleh Umar Saleh
Edita : Umaru Aliyu