1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Firaministan Lesotho ya sauka daga mukaminsa

May 19, 2020

Firaministan kasar Lesotho Thomas Thabane ya yi murabus, a wani mataki na yar da kwallon mangwaro don ya huta da kuda bisa zargin kisan kai.

https://p.dw.com/p/3cTyu
Lesothos Premierminister Thabane
Hoto: Reuters/F. Lenoir

Murabus din Thabane na zuwa ne bayan watanni uku da 'yan sanda suka ambaci sunansa da shi matarsa a cikin wani laifin kisan kai da aka aikata a kasar da ke kusa da Afirka ta Kudu. Tun farko 'yan sanda sun zarge shi da hada baki da matarsa ta yanzu wurin kisan tsohuwar matarsa, a shekara ta 2017, kwana biyu bayan ya dare kujerar Firaminista. Lamarin dai ya haifar da zazzafar muhawara a kasar.

An kuma ta matsa mi shi lamba a kan wannan zargi ta kowane bangare. Sai dai a jawabin da ya yi wa 'yan Lesotho a wannan Talata koda sau daya bai ambaci batun kisan kan da ake zarginsa da aikatawa ba. 

 ''Ya 'yan uwana 'yan Lesotho na tsaya yau a gabanku don in sanar da ku cewa watakila ban kammala aikin da kuka dora a kafadata ba, amma lokaci ya yi da zan janye jigi daga harkar shugabanci . Ina rokon ku da ku ba wanda zai gajeni goyon baya yadda ya kamata.'' inji tsohon firaministan.


An sanar da nadin Ministan Kudin kasar Dr Moeketsi Majoro a matsayin sabon Firaministan kasar ta Lesotho.