1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Garkuwa bisa dalilan siyasa a Libiya

Jane McintoshNovember 18, 2013

Sace-sacen manyan jami'an gwamnati na neman zama ruwan dare a Libiya inda a karo na biyu cikin watanni biyu, aka sake sace wani mai rike da babban mukami a kasar.

https://p.dw.com/p/1AJFf
Members of the security forces are seen outside the appeals court in Tripoli during the pre-trial hearing of ex-intelligence chief Abdullah Senussi and more than 20 former regime officials, accused of crimes during the 2011 revolt, on September 19, 2013. An AFP journalist said Senussi and more than 20 former regime officials appeared in court in the capital amid heavy security while Seif al-Islam Kadhafi, son of slain dictator Moamer Kadhafi, stood briefly in the dock before a judge adjourned his case in the western town of Zintan. AFP PHOTO / MAHMUD TURKIA (Photo credit should read MAHMUD TURKIA/AFP/Getty Images)
Hoto: M.Turkia/AFP/GettyImages

Wasu 'yan bindiga a kasar Libiya da ba a kai ga sanin ko su wanene ba sun sace mataimakin shugaban hukumar leken asirin kasar Mustafa Noah, wanda ba ya tare da jami'an tsaro dake yi masa rakiya a lokacin da aka sace shin, a wajen Filin sauka da tashin jiragen sama na Tripoli bayan dawowarsa daga bulaguro a kasashen ketare. Kawo yanzu babu wani ko wata kungiya da ta dauki alhakin sace shin ba, sannan ba a kai ga sanin inda ya ke ba.

Idan dai za a iya tunawa a watan Oktoban da ya gabata ne wasu 'yan bindiga suka sace firaminstan kasar Ali Zaidan, kafin daga bisani su sako shi bayan da aka kwashe tsahon wasu sa'oi. Shugabanni a Tripoli babban birnin kasar sun bukaci da a shiga wani yajin aiki na gama gari domin tilastawa gwamnatin kasar kan ta dakile ayyukan 'yan bindiga na sa kai, da ake dorawa alhakin rikicin da ya faru a makon jiya da yayi sanadiyyar mutuwar a kalla mutane 46.

Mawallafiya: Lateefa Mustapha Ja'afar
Edita: Mouhamadou Awal Balarabe