1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Garkuwa da Baki a arewacin Najeriya

February 17, 2013

'Yan bindiga sun yi garkuwa da 'yan kasashen ketere a garin Jama'are cikin Jihar Bauchi ta Najeriya

https://p.dw.com/p/17fle
A picture taken on April 18, 2011 shows Nigerian police enforcing a curfew in the capital of Bauchi state, nothern Nigeria, after riots, run by muslim youth, broke out in Bauchi. Nigeria's Goodluck Jonathan has been declared winner of presidential elections in a landmark vote that exposed regional tensions and led to deadly rioting in the mainly Muslim north. Jonathan, the incumbent and first president from the southern oil-producing Niger Delta region, won 57 percent of the vote in Africa's most populous nation, easily beating his northern rival, ex-military ruler Muhammadu Buhari. AFP PHOTO / Tony KARUMBA (Photo credit should read TONY KARUMBA/AFP/Getty Images)
Hoto: Getty Images/AFP

'Yan bindiga sun yi garkuwa da 'yan kasashen ketere bakwai, a garin Jama'are da ke Jihar Bauchi, a yankin arewa maso gabashin Tarayyar Najeriya.

Babban jami'in 'yan sandan jihar Mohammed Ladan ya tabbatar da faruwan lamarin. 'Yan sanda sun ce 'yan bindigan sun yi garkuwa da 'yan kasar Lebanon hudu, daya dan Birtaniya, dan Italiya, sannan dayan dan Girka. 'Yan sanda sun ce lamarin ya faru da sanyin safiyar wannan Lahadi (17.02.2013).

Yankin arewacin kasar ta Najeriya ya fuskancin matsalolin tsaron cikin shekarun da su ka gabata, abun da ya janyo mutuwan dubban mutane cikin hare haren 'yan bindiga da ake dangantawa da kungiyar Boko Haram mai gwagwarmaya da makamai.

Mawallafi: Suleiman Babayo
Edita: Saleh Umar Saleh