1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Gidauniyar taimakawa ƙasar Mali

February 5, 2013

Taron gamayyar ƙasa da ƙasa a birnin Brussels domin laluben hanyoyin warware rikicin ƙasar Mali

https://p.dw.com/p/17Y7E
France's President Francois Hollande (L) is welcomed by Mali's interim president Dioncounda Traore upon his arrival at Sevare, near Mopti, on February 2, 2013. President Francois Hollande visits Mali as French-led troops work to secure the last Islamist stronghold in the north after a lightning offensive against the extremists. Hollande will head to Timbucktu and Bamako. AFP PHOTO / PASCAL GUYOT (Photo credit should read PASCAL GUYOT/AFP/Getty Images)
Hoto: Pascal Guyot/AFP/Getty Images

Yau ne wakilai daga ƙasashe 45, tare da ƙungiyoyn bada agaji na ƙasa da ƙasa ke shirya zaman taro a birnin Brussels na ƙasar Beljiyam domin tunanin hanyoyin taimakawa ƙasar Mali.Majalisar Dinkin Duniya tare da haɗin gwiwar ƙungiyar gamayyar Afrika da ECOWAS su ka shirya wannan taro da zumar musanyar ra'ayoyin wanda za su fidda Mali daga halin da ta tsincin kanta, hasali ma, maida ƙasar bisa inganttatar turbar demokraɗiya, da kuma taimakawa dubunan 'yan gudun hijira da suka ƙauracerwa gidajensu.

A yanzu haka dai sojojin Mali tare da taimakon Faransa na cigaba da samun nasarori akan ƙungiyoyi da suka mamaye arewacin Mali.A nata ɓangare ƙungiyar Tarayya Turai ta yi alƙawarin aika tawagar ƙurrarun sojoji, domin horar ga dakarun Mali.

Mawallafi: Yahouza Sadissou Madobi
Edita: Usman Shehu Usman