1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Ghana: Za a kashe dala miliyan 200 a gina majalisa

Abdul-raheem Hassan
July 4, 2019

Gwamnatin kasar Ghana ta kare shirinta na kashe dala miliyan 200 kan aikin gina sabuwar majalisar dokokin kasar, duk da adawa da kudirin ke fuskanta daga al'umma.

https://p.dw.com/p/3LbEQ
Parlament in Accra, Ghana
Hoto: DW/I. Kaledzi

Kungiyoyin fararen hula sun kaddamar da kamfe a yanar gizo mai taken #Dropthatchanber wato a jingine batun gina sabuwar majalisa. A cewar kungiyoyin akwai muhimman bukatu da suka sha gaban ginda sabuwar majalisa.

Hukumomi a kasar Ghana na da muhimmanci domin fadada kujerun majalisar daga 275 zuwa kujeru sama da 400. Kasar ta Ghana za ta ranto kudaden aiwatar da aikin ne daga kasar Indiya. Sai dai batun na cigaba da haifar da muhawara tsakanin 'yan kasar da wajen kasar.