1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Girka ta ki bude kofa ga 'yan gudun hijira

February 28, 2020

Rahotanni daga Girka na cewa mahukumta sun ce ba za su bar 'yan gudun hijira su shigo ba tare da izini ba, Kuma za su kara tsaurara sintiri na musamman a iyakokinsu domin ganin babu wani dan gudun hijira da ya shigo.

https://p.dw.com/p/3Yc7d
Türkei Provinz Hatay | Grenze zu Syrien | Cilvegözü Border Gate
Hoto: DW/S. Görer

Rahotanni suka ce akwai 'yan gudun hijira 300 ciki har da mata da kananan yara da ke kan hanyarsu ta zuwa Girka bayan sun kaurace wa muhallinsu a yankin Idlib na Siriya. Amma Firaministan kasar Girka Kyriakos Mitsotakis ya ce ba za ta sabu ba.

Yan gudun hijira dai sun fara taruruwa a kan iyakar Girka da ke kusa da kasar Turkiyya ne bayan da suka sami labarin cewa Turkiyya ta yi barazanar bude iyakarta ga masu son zuwa nahiyar Turai.

To amma Firaministan ya ce kasar Girka ba ta da hannu a cikin rikicin Siriya, a don haka bai kamata a kawo mata wata dawainiya ta 'yan gudun hijira ba,