1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Gobara ta halaka majinyata Corona a Masar

Abdul-raheem Hassan
December 26, 2020

Mutane bakwai da ke jinyar cutar Corona sun mutu bayan da wuta ta tashi a asibitin da suke karbar jinya a birnin Alkahira na Masar. Sai dai ba a san me ya haddasa gobarar ba tukuna.

https://p.dw.com/p/3nEpV
Ägypten Kairo | Coronavirus | Medizinische Mitarbeiter
Hoto: picture-alliance/Photoshot/A. Gomaa

Masu fama da cutar Corona akalla bakwai sun mutu a Masar sakamakon tashin gobara a asibitin da ake jinyan marasa lafiya a kusa da babban birnin Alkahira.

Hukumomin sun tabbatar da karin wasu mutane akalla biyar da gobarar ta jikkata, ba a gano musabbabin tashin gobarar a asibitin ba, amma jami'an kashe gobara sun shawo kan matsalar.

A watan Yuni, wasu majinyata sun mutu a wani asibitin shi ma inda gobara ta tashi yayin da wasu da dama suka jikkata.