1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Halinda ake ciki a Gaza bayan tsagaita wuta

Usman ShehuNovember 22, 2012

Bayan tsagaita wuta a rikicin Gaza, jama'a na ci gaba da shagulgula a birnin don nuna murna

https://p.dw.com/p/16oGa
Palestinians celebrate the beginning of the truce with Israel in Rafah town in the southern Gaza Strip on November 21, 2012. Palestinians in Gaza took to the streets to celebrate the start of a truce deal with Israel that was announced in Egypt on the eighth day of violence in and around Gaza. AFP PHOTO/SAID KHATIB (Photo credit should read SAID KHATIB/AFP/Getty Images)
Palsdinawa ke murna a GazaHoto: SAID KHATIB/AFP/Getty Images

Sanar da tsagaita wuta ke da wuya, sai Palasdinawan zirin Gaza suka bazama kan tituna don shagulgulan murnar abin da suka kira "Nasarar da suka yi ta gagarar makiya" duk da rasa rayukan yan uwansu 160 da sukai da jikkatar daruruwa.

Titunan zirin na Gaza, wanda kwanson makaman da jiragen isra'ila suka yi ta harbawa ke warwatse kansu, sun cika makel da daruruwan masu shagulgulan kawo karshen hare haren kwanaki takwas da Isra'ila ta kai kan zirin na Gaza

Masu bukukuwan da suka daga tutocin kungiyar Hamas da hotunan wadanda suka kwanta dama sakamakon har haren, sun ce wannan biki na dukkan larabawa da musulmin duniya ne dama illahirin al'umomin da ke fuskantar danniyya.

A Hamas police officer is hugged by a Palestinian man after they returned to their destroyed police headquarters in Gaza City November 22, 2012. A ceasefire between Israel and Gaza's Hamas rulers took hold on Thursday after eight days of conflict, although deep mistrust on both sides cast doubt on how long the Egyptian-sponsored deal can last. REUTERS/Suhaib Salem (GAZA - Tags: CONFLICT POLITICS)
Palasdinawa ke taya juna murnar tsagaita wutaHoto: Reuters

"Tada kayar baya, da kin mika wuya ga azzalimai shi ya sa ake ganinmu da kima a idanun duniya, mu a wajenmu da kaskanci gwanda shahada, kuma da yardarm Allah sai mun kwato masallacin Kudus da Isra'ila ta mamaye munyi sallah cikinsa"

Su kuwa wadanda yakin ya jefa cikin halin kakani ka yi, ko kuwa suka rasa danginsu, wadannan shagulgula da ake yi bai hanasu ci gaba da yin makaoki da la'antar wadanda suka yi wa danginsu sanadi ba.

Kamar dai yadda Isra'ilan ke ikirari, hare haren nata sunyi nasarar ragargaza illahirin karfin makaman kungiyoyi masu tada kayar baya dake zirin na Gaza, ikirarin da jagororin Hamas suka musanta. Suna masu cewa, har yanzu rumbun makamansu nanan cike makel da makaman da kasar Iran ta basu, da kuma wadanda suka kera da kansu, kuma a shirye suke da su sake fafatawa da Isra'ilan a duk lokacin da ta takale su.

Israeli Prime Minister Benjamin Netanyahu sits next to Defence Minister Ehud Barak during a statement to the press at his Jerusalem office on November 21, 2012. Israel and Hamas agreed on a truce that will take effect this evening in a bid to end a week of bloodshed in and around Gaza that has killed more than 150 people, Egypt and the United States said. AFP PHOTO/GALI TIBBON (Photo credit should read GALI TIBBON/AFP/Getty Images)
Firayim ministan Isra'ila Benjamin Netanyahu da ministan tsaronsa Ehud BarakHoto: GALI TIBBON/AFP/Getty Images

Ana su bangaren, masu tsatsauran ra'ayi na bani Yahudu na ganin cewa, gwamnatin Natayanhu ta basu kunya da ta ba da kai bori ya hau, har ta yi sulhu da Hamas.

" Ada an mayar da Hamas saniyar ware, amma tun da aka fara yakin na sai muka ga yawancin kasashen duniya na sake tausaya mata, kai har wasu shuwagabannin larabawa ma suka yi ta kai mata ziyara, kamar yadda muka yadda da tattaunawa da ita a fakaice, dole ne ma a yanzu Hamas ta dauki kanta a matsayin gwarzon kasashen larabawa"

Kamar dai yadda masharhanta ke gani, bawa Palasdinawa kasar kansu, da kuma taimaka musu da isassun makamai shine kadai zai iya magance irin ta'annutin da Isra'ila ke musu.

Mawallafi: Mahmud Yaya Azare

Edita: Usman Shehu Usman