1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Holland: An kai hari a tashar jirgin kasa

Yusuf Bala Nayaya
March 18, 2019

A cewar jami'an 'yan sandan, harin da aka kai a birnin Utrecht shi ya zaburar da mahukunta daukar matakai na tsaurara tsaro .

https://p.dw.com/p/3FFNw
Verletzte nach Schießerei in Utrecht
Hoto: Reuters/P. van de Wouw

Kasar Holland ta tsaurara matakan tsaro a filayen tashi da saukar jiragen sama na kasar da ma wasu manyan gine-gine bayan da wani dan bundiga ya bude wuta a tashar jirgin kasa da ma kisan mutane guda uku baya ga wasu da dama da suka samu raunika kamar yadda jami'an 'yan sanda a kasar suka bayyana.

A cewar jami'an 'yan sandan, harin da aka kai a birnin Utrecht shi ya zaburar da mahukunta daukar matakai na tsaurara tsaro a manyan gine ginen a kasar ta Holland.