1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Harin Boko Haram a Jihar Adamawa ta Najeriya

Ahmed SalisuOctober 19, 2015

Fiye da mutane 10 sun rasu sakamakon wani hari da wasu 'yan bindiga da ake zaton 'yan kungiyar nan ta Boko Haram ne suka kai kauyen Dar da ke Jihar Adamawa ta Najeriya.

https://p.dw.com/p/1GqEA
Nigeria Boko Haram Terrorist
Hoto: picture alliance/AP Photo

Hukumar ba da agajin gaggawa ta kasar NEMA da ta tabbatar da wannan labarin ta ce an kai harin ne a karshen mako sai dai ba ta yi karin haske ba dangane da lamarin ba.

Wadanda suka shaida faruwar wannan lamari dai sun ce mutane bakwai daga cikin mutanen sun rasu ne bayan da wasu mata biyu suka tada bam din da yake jikinsu, yayin da sauran kuma suka gamu da ajalinsu sanadiyyar harbi da bindiga da aka yi musu.

Jihar Adamawa dai tana daga cikin jihohin da ke yankin arewa maso gabashin Najeriya da tada kayar bayan 'yan kungiyar ta Boko Haram ke shafa, batun da ya yi sanadin rasuwa dubban mutane.