1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Harin kunar bakin wake kan 'yan kungiyar IS

Ahmed SalisuOctober 5, 2014

Wata mata ta tada bam da ta sanya a jikinta daidai inda 'yan kungiyar nan ta IS suke a garin Kobani da ke kan iyakar Siriya da Turkiyya.

https://p.dw.com/p/1DQ8B
Pakistan Anschlag mit einer Autobombe in Quetta 13.09.2014
Hoto: AFP/Getty Images/B. Khan

Hukumar da ke sanya idanu kan kare hakkin dan Adam a Siriya wato Syrian Observatory for Human Rights ta ce matar ta tada bam din ne a gabashin garin na Kobani inda 'yan IS da ke son karbe garin suka ja daga kuma harin ya hallaka 'yan kungiyar da dama.

Ya zuwa yanzu dai ba a tantance yawan wanda suka rasu ko suka jikkata ba. Wannan dai shi ne karon farko da Kurdawa musamman ma dai mace ta kai harin kunar bakin wake kan 'yan kungiyar ta IS.