1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Harin kunar bakin wake ya hallaka mutane 10 a Somaliya

Suleiman BabayoApril 21, 2015

A Somaliya harin kunar bakin wake da mota mai dauke da bam ya hallaka mutane 10

https://p.dw.com/p/1FBxs
Terroranschlag in Mogadischu, Somalia
Hoto: M. Abdiwahab/AFP/Getty Images

Wani dan harin kunar bakin wake ya hallaka kimanin mutane 10, lokacin da ya tashi bam cikin mota a wajen cin abinci mai cike da mutane da ke tsakiyar birnin Mogadishu fadar gwamnatin kasar Somaliya. Harin na wannan Talata an kai shagon cin abinci da ma'aikata ke zuwa.

'Yan sanda sun ce akwai yuwuwar samun karin wadanda za su halaka saboda akwai wadanda suka samu munanan raunika. A jiya Litinin wani hari kan ma'aikatan Majalisar Dinkin Duniya ya kai ga mutuwar mutane bakwai. Ana daura alhakin hare-haren da ake samu a kasar ta Somaliya kan tsagerun kungiyar al-Shabaab masu kaifin kishin addinin Islama.