1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Zanga-zangar Indiya ta lashe rayuka

Binta Aliyu Zurmi
February 26, 2020

Rahotanni daga kasar Indiya na nuni da cewar adadin wadanda suka mutu a rikicin kasar ya haura zuwa mutane 27, yayin da sama da wasu 200 suka jikkata.

https://p.dw.com/p/3YU2f
ndien Neu Delhi Proteste gegen Staatsbürgerschaftsgesetz
Hoto: Getty Images/AFP/S. Hussain

Firaministan Indiyan, Narendra Modi ya bukaci al'ummar kasar da su kwantar da hankula a kan boren da ke ci gaba da daukar sabon salo. Wannan dai shi ne bore mafi muni da birnin na New Delhi ke fuskanta, a dangane da haka ne ma Mr Modi ya bukaci sojoji da su saka dokar hana fita a birnin.

Tun a watan Disambar shekarar da ta gabata ne al'ummar kasar ta Indiya ke boren adawa da sabuwar dokar dan kasa, inda suke ta dauki-ba-dadi da jami'an tsaro. Musulmi da dama ne wannan rikicin ya tilsata musu barin gidajensu yayin da aka kona wasu masallatai a birnin na New Delhi.